Site icon Samaniya Reporters

RANAR DA KOWA YAKE TA KANSA.

RANAR DA KOWA YAKE TA KANSA.

“Allah maɗaukakin sarki ya laburta mana yadda kowa yake yin takansa a ranar ƙiyamah, kowa burinsa idanma kowa zai halaka to shi ya tserata. A ranar ne uwa za ta ajiye ɗan da ta haifa, uba zai guji matarsa da ƴaƴansa, a ranar shima ta kansa yake babu batun ya taimaki iyalinsa”

“Ranar da mutum yake gudu daga ɗan-uwansa, da uwarsa da ubansa, da matarsa da ɗiyansa, ga kowane mutum daga cikinsu, a ranar nan akwai wani sha’ani da ya ishe shi” (Surah Abasa)

“A ranar lahira kowa yakan zamto neman takansa yake yi, babu mai lura da halin da ɗan-uwansa yake ciki, kowa burinsa ya samu tsira a wannan ranar. Ɗan-uwa yakan guji ɗan-uwansa. Ɗa yakan guji uwarsa da ubansa. Uwa takan tsallake ta bar ɗanta. Kowa yakanyi ta kansa ne a wannan ranar, babu mai taimakon wani don wani ya tserata. Haƙiƙa wannan ya ishi mai hankali tashin hankali game da sha’anin wannan ranar”

Exit mobile version